Fatwa

Islamic legal opinions and answers to your questions

assalamu alaikum Mallam shin ko yahalatta mutum yayi nafila kafin sallah magrib

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 20, 2026 Answered

Wa alaikum slm, ya halatta, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya kwaÉ—aitar

assalamualaikum mlm ya hukuncin wadda ya wadda karanta falaqi da nasi bayan sallar asuba amma dayazo yin azkar sai karantasuba yawuce shin ya mastayin azkhar nashi yayi

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 20, 2026 Answered

Wa alaikum slm, ko wanne zai karanta su, na bayan sallah daban da na Azkar É—in safe

assalamu alikum warahamatullah tambaya na shine idan mutum ya samu raka a daya a Sallah mangariba yaya zai yi ya cika sallarsa bayan liman ya iddar

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 08, 2026 Answered

Zai tashi ya kawo raka'a É—aya sura da Fatiha a bayyane, sai yayi tahiya ya sake tashi ya kawo raka'a É—aya Fatiha zalla. Wallahu Ta'ala A'alam

assalamu alaikum Mallam wane lokaci matar da tahaihu yakamata tafara sallah shin lallene harsai tayi kwana 40 ko ko

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 08, 2026 Answered

Wa alaikum slm, ba dole sai tayi kwana 40 ba, idan jinin haihuwar ta ya É—auke koda a ranar da ta haihu ne zata fara sallah. Dama ai jinin shine yasa aka mata rangwamen sallah. Wallahu Ta'ala A'alam

assalamu alaikum Mallam gawanda yake dawata lalura ga kafa indan yazo alwala shin doline sai yawanke inda Babu lalura ko zai iya barinta indan yaga zai cutu nagode Mallam

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 08, 2026 Answered

Wa alaikum slm, iya inda ke da lalura ne ba zai wanke ba, sauran wajen dole zai wanke

Aslm, Alaykum malam ubangiji Allah ya sa agama da duniya lafiya, ya kuma albarkaci zuriya ya jikan iyayen mu. malam shin mutum zai iya yin abunda mahaifiyarsa ta yarje masa yayi amma mahaifinsa bai yadda ba? kuma bai saɓawa shari'a ba? wsslm

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 08, 2026 Answered

Wa alaikum slm warahmatullah, Allah ya amsa addu'a. Da so samu ne duk ya nemi yardar su, idan har abin ba na dole bane, Gara ya hakura domin kowa a cikin su yana haƙƙin biyayya. ko kuma yayi ƙoƙarin fahimtar da shi mahaifin. Wallahu Ta'ala A'alam

ASSALAM ALAIKUM MALAM nine ina son karatun islamiyya amma yanzu kuma aiki ya samu shine iyayena kuma sun fi son na dinga zuwa aikin da na dinga zuwa makaranta ni kuma na fi son zuwa makaranta da zuwan wajen aiki amma daga baya ne nace zan dinga tasowa Daga aiki Da wuri don na kama zuwa makaranta nafara haka amma yanzu zuwa shagon Ya hana ya zanyi yanzu

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 08, 2026 Answered

Wa alaikum slm, neman ilimin addini wajibi, babu wani abu da hana wajibcin sa. Idan ba ilimi, bautar Allah ma ba zata karɓu ba. Dole ka samar wa kanka wani lokaci da zaka je makaranta, idan kuma zuwa makaranta ba zai yiwu ba, ka nemi malami da zaka din ga zuwa kana ɗauka a lokacin da kake da sarari

Assalamualaikum warahmatullah mlm.minene hukuncin ciki na order

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 08, 2026 Answered

Wa alaikum slm warahmatullah, ban gane tambar ba. Amma idan tana nufin ciniki da ake na order, ya halatta idan kasan siffan da dukkan bayanai akan kayan da zaka saya. Wallahu Ta'ala A'alam

Assalamu alaikum, inawa Mlm fatan alkairi, Mlm ina d tambaya shin yin addu'a d hausa yayi sujudi y halatta. Allah karawa Mlm lfy amen

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 08, 2026 Answered

Wa alaikum slm, fatan alkhairi zuwa ga É—an uwa. Wasu malamai sun ce ya halatta, amma ka dage ka koyi larabci, ko kuma ka haddace waÉ—an da Manzon Allah ya koyar. Wallahu Ta'ala A'alam

hukunchin sanya tozali ga namiji

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 08, 2026 Answered

Ya halatta

shi yaro Wanda yake ba musulmi bane ze iya cin gadon baban sah musulmi

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 02, 2026 Answered

A zahirin Hadisin Manzon Allah ya nuna Musulmi baya cin gadon Wanda ba musulmi ba, haka shima wanda ba musulmi ba baya cin gadon Musulmi. Amma idan akwai wata maslaha shi musulmi zai iya cin gadon iyayensa wanda ba musulmai ba. Shawara kawai aje kotun musulunci domin samun natsuwa. Wallahu Ta'ala A'alam

Assalamu'alaikum Warahmatullah. Barka da wannan lokacin fatan kana cikin, Allah yasa haka. Tambaya anan shine Azumin guda uku da akeyi ko wani wata na 13, 14, 15 to misali ka fara kayi biyu sai wani masala yasa baka samu kayi na ukun a jere ba so yanzu idan zakayi sabo zaka sake kodai dayan daya saura zakayi. Allah Ta'ala ya Bada Ikon Amsawa🙏

Copied!
Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman • Jul 02, 2026 Answered

Wa alaikum slm warahmatullah. Idan na fahimta, me tambaya na nufin azumin ranakun hasken wata (Ayyamul Beed) wanda Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya kwaÉ—aitar. Idan mutum ya fara sai matsala ta bujiro, to iya wanda yayi shikenan sai kuma wani wata. Dama azumin nafila ne ba Farilla ba, saboda haka ba wani biya da yake kansa. Wallahu Ta'ala A'alam