Question

Copied!

Assalamu'alaikum Warahmatullah. Barka da wannan lokacin fatan kana cikin, Allah yasa haka. Tambaya anan shine Azumin guda uku da akeyi ko wani wata na 13, 14, 15 to misali ka fara kayi biyu sai wani masala yasa baka samu kayi na ukun a jere ba so yanzu idan zakayi sabo zaka sake kodai dayan daya saura zakayi. Allah Ta'ala ya Bada Ikon Amsawa🙏

Asked by: Alhassan Mohammed Adamu

Answer

Answered by: Ustadh Auwal Abdullahi Usman

Wa alaikum slm warahmatullah. Idan na fahimta, me tambaya na nufin azumin ranakun hasken wata (Ayyamul Beed) wanda Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya kwaɗaitar. Idan mutum ya fara sai matsala ta bujiro, to iya wanda yayi shikenan sai kuma wani wata. Dama azumin nafila ne ba Farilla ba, saboda haka ba wani biya da yake kansa. Wallahu Ta'ala A'alam

Answered on July 02, 2026

Answered

Related Fatwa

assalamu alaikum Mallam shin ko yahalatta mutum yayi nafila kafin sallah magrib

Wa alaikum slm, ya halatta, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya kwaɗaitar

Read Full Answer →

assalamualaikum mlm ya hukuncin wadda ya wadda karanta falaqi da nasi bayan sallar asuba amma dayazo...

Wa alaikum slm, ko wanne zai karanta su, na bayan sallah daban da na Azkar ɗin safe

Read Full Answer →

assalamu alikum warahamatullah tambaya na shine idan mutum ya samu raka a daya a Sallah mangariba ya...

Zai tashi ya kawo raka'a ɗaya sura da Fatiha a bayyane, sai yayi tahiya ya sake tashi ya kawo raka'a ɗaya Fatiha zalla. Wallahu Ta'ala A'alam

Read Full Answer →

assalamu alaikum Mallam wane lokaci matar da tahaihu yakamata tafara sallah shin lallene harsai tayi...

Wa alaikum slm, ba dole sai tayi kwana 40 ba, idan jinin haihuwar ta ya ɗauke koda a ranar da ta haihu ne zata fara sallah. Dama ai jinin shine yasa a...

Read Full Answer →

assalamu alaikum Mallam gawanda yake dawata lalura ga kafa indan yazo alwala shin doline sai yawanke...

Wa alaikum slm, iya inda ke da lalura ne ba zai wanke ba, sauran wajen dole zai wanke

Read Full Answer →

Aslm, Alaykum malam ubangiji Allah ya sa agama da duniya lafiya, ya kuma albarkaci zuriya ya jikan i...

Wa alaikum slm warahmatullah, Allah ya amsa addu'a. Da so samu ne duk ya nemi yardar su, idan har abin ba na dole bane, Gara ya hakura domin kowa a ci...

Read Full Answer →